29 Mayu 2021 - 14:15
​Rwanda Da Faransa Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Fahintar Juna Tsakanin Kasashen Biyu

Gwamnatocin kasashen Faransa da Ruwanda sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahintar juna tsakanin kasashen biyu, wanda suke daukarsa a matsayin bude wani sabon shafi a dangantarkar kasashen biyu.

ABNA24 : Jaridar Time Line ta kasar Ruwanda ta bayyana cewa ministan harkokin wajen na kasar Faransa Jean –Yves Le Drian da tokoransa na kasar Ruwanda Vincent Biruta ne suka sanya hannu a kan yarjejeniyar a gaban shuwagabannin kasashen biyu.

Banda haka gwamnatin kasar Faransa ta nuna alluran riga kafin cutar korona 100,000 wanda shugaban kasar ta Faransa ya zo da su a cikin jirginsa a matsayin tallafi ga kasar Ruwanda don yaki da cutar.

Har’ila yau kasashen biyu san sanya hannu a kan yarjejeniyar aiki tare a fagen wasannin da watsa kwakwalwa wanda zai bawa Ruwanda damar karban uoro miliyon E1.5 daga kasar Faransa.

Kafin haka, a bangaren raya kasa samar da ayyukan yi kuma kasashen biyu sun rattabawa hannu kan bashin uoro miliyon 60.

342/